Idan kare ya sha a kwaryar ɗayanku to ya wanketa sau bakwai
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan kare ya sha a kwaryar ɗayanku to ya wanketa sau bakwai". A riwayar Muslim: "Na farkonsu da turbaya".

