Kada harshenka ya gushe yana ɗanye daga ambatan Allah
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abdullahi ibnu Busr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum Ya zo wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya ce: Ya Manzon Allah! Lallai cewa shari'un Musulunci sun yawaita a kanmu, to wace ƙofa ce mai tattarowa zamu yi riƙo da ita? ya ce: «Kada harshenka ya gushe yana ɗanye daga ambatan Allah». A cikin wata riwayar: Daga hadisin Mu'azu ibnu Jabal - Allah Ya yarda da shi -: Ƙarshen abin da na rabu da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a kansa shi ne na ce: Wane aiki ne daga cikin ayyuka ya fi kuma ya fi kusanci zuwa ga Allah? Ya ce: «Ka mutu alhali harshenka yana ɗanye daga ambatan Allah».
Explanation
Sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya nunar masa harshensa ya zama ɗanye mai motsawa saboda dawwamar ambatan Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - a kowane lokaci da hali; na tasbihi da tahmidi da istigafari da addu'a da makamancin hakan.
Benefits
Daga girman falalar Allah (akwai) sawwaƙe sabubban lada.
Fifikon bayi a rabonsu na ƙofofin aikin lada da alheri.
Yawan ambatan Allah da harshe tasbihi da tahmidi da hailala da kabbara da wanin hakan, tare da dacewar zuciya yana tsayawa matsayin yawa da yawan nafilifilin ayyukan ɗa'a.
Lurarsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ga masu tambaya da amsawa kowa da abinda ya dace da shi.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

