Na haɗu da (Annabi) Ibrahim a daren da aka yi Isra'i dani sai ya ce: Ya Muhammad, ka yi wa al'ummarka sallama daga gareni, kuma ka basu labarin cewa aljanna mai daɗin turɓaya ce mai daɗin ruwa ce
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Na haɗu da (Annabi) Ibrahim a daren da aka yi Isra'i dani sai ya ce: Ya Muhammad, ka yi wa al'ummarka sallama daga gareni, kuma ka basu labarin cewa aljanna mai daɗin turɓaya ce mai daɗin ruwa ce, kuma ita faƙo ce kuma dashenta (shi ne): Subhanallah, (tsarki ya tabbata ga Allah), Alhamdulillah (godiya ta tabbata ga Allah), Lailaha Illallahu, (babu abin bautawa da gaskiya sai Allah), Allahu Akbar (Allah ne Mafi girma)".
Explanation
Benefits
Falalar al'ummar musulmi; inda (Annabi) Ibrahim - tsira da aminci su tabbata agare shi - ya isar mata da sallama.
Kwaɗaitarwa (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - ga al'ummar (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cikin yawaitawa daga ambatan Allah - Maɗaukakin sarki -.
Malam al-Ɗaibi ya ce: Aljanna ...?, sannan Allah - Maɗaukakin sarki - Ya samar mata da bishiyoyi da katangu da falalarsa gwargwdan ayyukan masu aiki; kowane mai aiki akwai abinda ya keɓanta da shi saboda aikinsa, sannan cewa Shi - Allah Maɗaukakin sarki - yayin da Ya sawwaƙa masa dan abinda Ya halicce shi saboda shi na aiki dan ya samu lada da hakan sai Ya sanya shi kamar mai dasa waɗancan bishiyoyin.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

