Wanda ya gangaro daga wani dutse sai ya kashe kansa to shi yana cikin wuta zai dinga gangarowa a cikinta yana abin dawwamarwa a cikinta har abada
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Wanda ya gangaro daga wani dutse sai ya kashe kansa to shi yana cikin wuta zai dinga gangarowa a cikinta yana abin dawwamarwa a cikinta har abada, wanda ya tsotsi wata gubar sai ya kashe kansa to gubarsa tana hannunsa zai dinga tsotsarta a cikin wutar Jahannama yana madawwami a cikinta har abada, wanda ya kashe kansa da wani ƙarfe to ƙarfen zai zama a hannunsa zai dinga cakawa cikinsa shi a cikin wutar Jahannama yana madawwami har abada a cikinta».
Explanation
Benefits
Abinda ya ambata a cikin hadisin buga misali ne ga wasu daga cikin nau'ikan kashe rai, inba haka ba to ta kowace hanaya ya kashe rai za’a yi masa uƙuba da kwatankwacin abinda ya aikatawa kansa, haƙiƙa faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo a cikin Sahihul Bukhari cewa: «Wanda ya shaƙe kansa zai shaƙe shi a cikin wuta, wanda kuma ya soke kansa to zai sokeshi a cikin wuta».
Nawawi ya ce: Amma faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: (To shi yana cikin wutar Jahanama yana madawwami a cikinta har abada); sai aka ce: A cikinsa akwai maganganu, na farkonsu: Cewa shi abin ɗauka ne akan wanda ya aikata hakan yana mai halattawa tare da saninsa da haramcin to wannan kafiri ne, wannan kuma ita ce uƙubarsa. Na biyu: Cewa abin nufi da dawwama ita ce tsawon dadewa da kuma zaman da za'a tsawaita ba wai haƙiƙanin dawwamar ba, kamar yadda ake cewa: Allah Ya dawwamar da mulkin sarki. Na uku: Cewa wannan shi ne sakamakonsa, sai dai (Allah) tsarki ya tabbatar maSa ya daukaka ya yi baiwa sai Ya bada labarin cewa wanda ya mutu yana musulmi ba zai dawwama a cikin wuta ba.
Wannan yana daga babin tabbatar da jinsin uƙubobin lahira ga laifukan duniya, kuma ana fahimta daga gare shi cewa laifin mutum yana kan kansa kamar laifin waninsa ne akan waninsa a zunubi; domin cewa ransa ba mallakinsa bane kai tsaye, kai shi na Allah ne - Maɗaukakin sarki -, ba'a tasarrufi a cikinsa sai da abinda Ya yi masa izini a cikinsa.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

