الفجر

 

Al-Fajr

 

The Dawn

1 - Al-Fajr (The Dawn) - 001

وَٱلۡفَجۡرِ
Inã rantsuwa da alfijiri.

2 - Al-Fajr (The Dawn) - 002

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ
Da darũruwa gõma.

3 - Al-Fajr (The Dawn) - 003

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

4 - Al-Fajr (The Dawn) - 004

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ
Da dare idan yana shũɗewa.

5 - Al-Fajr (The Dawn) - 005

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

6 - Al-Fajr (The Dawn) - 006

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

7 - Al-Fajr (The Dawn) - 007

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ
Iramawa mãsu sakon* ƙĩrar jiki.
* Tsawo mai ma'ana.

8 - Al-Fajr (The Dawn) - 008

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

9 - Al-Fajr (The Dawn) - 009

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi* suka yi gidãje)?
* Wãdil-ƙura, sunan wuri ne kusa da Madina wajen Syria, wato Sham.

10 - Al-Fajr (The Dawn) - 010

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ
Da Fir'auna mai turãku.

11 - Al-Fajr (The Dawn) - 011

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

12 - Al-Fajr (The Dawn) - 012

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

13 - Al-Fajr (The Dawn) - 013

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

14 - Al-Fajr (The Dawn) - 014

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

15 - Al-Fajr (The Dawn) - 015

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

16 - Al-Fajr (The Dawn) - 016

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

17 - Al-Fajr (The Dawn) - 017

كَلَّاۖ بَل لَّا تُكۡرِمُونَ ٱلۡيَتِيمَ
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

18 - Al-Fajr (The Dawn) - 018

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

19 - Al-Fajr (The Dawn) - 019

وَتَأۡكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكۡلٗا لَّمّٗا
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

20 - Al-Fajr (The Dawn) - 020

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

21 - Al-Fajr (The Dawn) - 021

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

22 - Al-Fajr (The Dawn) - 022

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, sahu- sahu.

23 - Al-Fajr (The Dawn) - 023

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

24 - Al-Fajr (The Dawn) - 024

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

25 - Al-Fajr (The Dawn) - 025

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

26 - Al-Fajr (The Dawn) - 026

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurin Sa.

27 - Al-Fajr (The Dawn) - 027

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ
Yã kai rai mai natsuwa!

28 - Al-Fajr (The Dawn) - 028

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

29 - Al-Fajr (The Dawn) - 029

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyi Na (mãsu bin umurui a dũniya).

30 - Al-Fajr (The Dawn) - 030

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

Scroll to Top