النبإ

 

An-Naba

 

The Tidings

1 - An-Naba (The Tidings) - 001

عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ
A kan mẽ suke tambayar jũna?

2 - An-Naba (The Tidings) - 002

عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلۡعَظِيمِ
A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

3 - An-Naba (The Tidings) - 003

ٱلَّذِي هُمۡ فِيهِ مُخۡتَلِفُونَ
Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

4 - An-Naba (The Tidings) - 004

كَلَّا سَيَعۡلَمُونَ
A'aha! Zã su sani.

5 - An-Naba (The Tidings) - 005

ثُمَّ كَلَّا سَيَعۡلَمُونَ
Kuma, a'aha! Zã su sani.

6 - An-Naba (The Tidings) - 006

أَلَمۡ نَجۡعَلِ ٱلۡأَرۡضَ مِهَٰدٗا
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

7 - An-Naba (The Tidings) - 007

وَٱلۡجِبَالَ أَوۡتَادٗا
Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

8 - An-Naba (The Tidings) - 008

وَخَلَقۡنَٰكُمۡ أَزۡوَٰجٗا
Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

9 - An-Naba (The Tidings) - 009

وَجَعَلۡنَا نَوۡمَكُمۡ سُبَاتٗا
Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

10 - An-Naba (The Tidings) - 010

وَجَعَلۡنَا ٱلَّيۡلَ لِبَاسٗا
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

11 - An-Naba (The Tidings) - 011

وَجَعَلۡنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشٗا
Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

12 - An-Naba (The Tidings) - 012

وَبَنَيۡنَا فَوۡقَكُمۡ سَبۡعٗا شِدَادٗا
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

13 - An-Naba (The Tidings) - 013

وَجَعَلۡنَا سِرَاجٗا وَهَّاجٗا
Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

14 - An-Naba (The Tidings) - 014

وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلۡمُعۡصِرَٰتِ مَآءٗ ثَجَّاجٗا
Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

15 - An-Naba (The Tidings) - 015

لِّنُخۡرِجَ بِهِۦ حَبّٗا وَنَبَاتٗا
Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

16 - An-Naba (The Tidings) - 016

وَجَنَّـٰتٍ أَلۡفَافًا
Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

17 - An-Naba (The Tidings) - 017

إِنَّ يَوۡمَ ٱلۡفَصۡلِ كَانَ مِيقَٰتٗا
Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

18 - An-Naba (The Tidings) - 018

يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِ فَتَأۡتُونَ أَفۡوَاجٗا
Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

19 - An-Naba (The Tidings) - 019

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ أَبۡوَٰبٗا
Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

20 - An-Naba (The Tidings) - 020

وَسُيِّرَتِ ٱلۡجِبَالُ فَكَانَتۡ سَرَابًا
Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

21 - An-Naba (The Tidings) - 021

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتۡ مِرۡصَادٗا
Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

22 - An-Naba (The Tidings) - 022

لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابٗا
Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

23 - An-Naba (The Tidings) - 023

لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحۡقَابٗا
Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

24 - An-Naba (The Tidings) - 024

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرۡدٗا وَلَا شَرَابًا
Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

25 - An-Naba (The Tidings) - 025

إِلَّا حَمِيمٗا وَغَسَّاقٗا
Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

26 - An-Naba (The Tidings) - 026

جَزَآءٗ وِفَاقًا
Sakamako mai dãcẽwa.

27 - An-Naba (The Tidings) - 027

إِنَّهُمۡ كَانُواْ لَا يَرۡجُونَ حِسَابٗا
Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

28 - An-Naba (The Tidings) - 028

وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كِذَّابٗا
Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyin Mu, ƙaryatãwa!

29 - An-Naba (The Tidings) - 029

وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ كِتَٰبٗا
Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

30 - An-Naba (The Tidings) - 030

فَذُوقُواْ فَلَن نَّزِيدَكُمۡ إِلَّا عَذَابًا
Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

31 - An-Naba (The Tidings) - 031

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا
Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

32 - An-Naba (The Tidings) - 032

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا
Lambuna da inabõbi.

33 - An-Naba (The Tidings) - 033

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا
Da yan Mata tsaraikun Juna

34 - An-Naba (The Tidings) - 034

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا
Da hinjãlan giya cikakku.

35 - An-Naba (The Tidings) - 035

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا
Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

36 - An-Naba (The Tidings) - 036

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا
Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

37 - An-Naba (The Tidings) - 037

رَّبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا ٱلرَّحۡمَٰنِۖ لَا يَمۡلِكُونَ مِنۡهُ خِطَابٗا
Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

38 - An-Naba (The Tidings) - 038

يَوۡمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ صَفّٗاۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَقَالَ صَوَابٗا
Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

39 - An-Naba (The Tidings) - 039

ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلۡحَقُّۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا
Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

40 - An-Naba (The Tidings) - 040

إِنَّآ أَنذَرۡنَٰكُمۡ عَذَابٗا قَرِيبٗا يَوۡمَ يَنظُرُ ٱلۡمَرۡءُ مَا قَدَّمَتۡ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلۡكَافِرُ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ تُرَٰبَۢا
Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

Scroll to Top