القيامة

 

Al-Qiyamah

 

The Resurrection

1 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 001

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ
Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba.
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.

2 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 002

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.

3 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 003

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

4 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 004

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

5 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 005

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

6 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 006

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

7 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 007

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

8 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 008

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

9 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 009

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ
Aka tãra rãnã da watã

10 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 010

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

11 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 011

كَلَّا لَا وَزَرَ
A'aha! bãbu mafaka.

12 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 012

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

13 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 013

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

14 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 014

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

15 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 015

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

16 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 016

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ
Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
* Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.

17 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 017

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

18 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 018

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

19 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 019

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

20 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 020

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

21 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 021

وَتَذَرُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

22 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 022

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاضِرَةٌ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

23 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 023

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٞ
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

24 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 024

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذِۭ بَاسِرَةٞ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

25 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 025

تَظُنُّ أَن يُفۡعَلَ بِهَا فَاقِرَةٞ
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

26 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 026

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِيَ
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

27 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 027

وَقِيلَ مَنۡۜ رَاقٖ
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

28 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 028

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلۡفِرَاقُ
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

29 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 029

وَٱلۡتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

30 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 030

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمَسَاقُ
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.
* Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.

31 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 031

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

32 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 032

وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

33 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 033

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

34 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 034

أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰ
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

35 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 035

ثُمَّ أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰٓ
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

36 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 036

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَن يُتۡرَكَ سُدًى
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

37 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 037

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ
Bai kasance ɗigo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

38 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 038

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

39 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 039

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

40 - Al-Qiyamah (The Resurrection) - 040

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?*
* Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.

Scroll to Top