الطور

 

At-Tur

 

The Mount

1 - At-Tur (The Mount) - 001

وَٱلطُّورِ
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).

2 - At-Tur (The Mount) - 002

وَكِتَٰبٖ مَّسۡطُورٖ
Da wani littãfi rubũtacce.

3 - At-Tur (The Mount) - 003

فِي رَقّٖ مَّنشُورٖ
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.

4 - At-Tur (The Mount) - 004

وَٱلۡبَيۡتِ ٱلۡمَعۡمُورِ
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).

5 - At-Tur (The Mount) - 005

وَٱلسَّقۡفِ ٱلۡمَرۡفُوعِ
Da rufin nan da aka ɗaukaka.

6 - At-Tur (The Mount) - 006

وَٱلۡبَحۡرِ ٱلۡمَسۡجُورِ
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).

7 - At-Tur (The Mount) - 007

إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٞ
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.

8 - At-Tur (The Mount) - 008

مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٖ
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.

9 - At-Tur (The Mount) - 009

يَوۡمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوۡرٗا
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.

10 - At-Tur (The Mount) - 010

وَتَسِيرُ ٱلۡجِبَالُ سَيۡرٗا
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.

11 - At-Tur (The Mount) - 011

فَوَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

12 - At-Tur (The Mount) - 012

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي خَوۡضٖ يَلۡعَبُونَ
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.

13 - At-Tur (The Mount) - 013

يَوۡمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.

14 - At-Tur (The Mount) - 014

هَٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."

15 - At-Tur (The Mount) - 015

أَفَسِحۡرٌ هَٰذَآ أَمۡ أَنتُمۡ لَا تُبۡصِرُونَ
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"

16 - At-Tur (The Mount) - 016

ٱصۡلَوۡهَا فَٱصۡبِرُوٓاْ أَوۡ لَا تَصۡبِرُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡكُمۡۖ إِنَّمَا تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

17 - At-Tur (The Mount) - 017

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَعِيمٖ
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.

18 - At-Tur (The Mount) - 018

فَٰكِهِينَ بِمَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ وَوَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.

19 - At-Tur (The Mount) - 019

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

20 - At-Tur (The Mount) - 020

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ سُرُرٖ مَّصۡفُوفَةٖۖ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.

21 - At-Tur (The Mount) - 021

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱتَّبَعَتۡهُمۡ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَٰنٍ أَلۡحَقۡنَا بِهِمۡ ذُرِّيَّتَهُمۡ وَمَآ أَلَتۡنَٰهُم مِّنۡ عَمَلِهِم مِّن شَيۡءٖۚ كُلُّ ٱمۡرِيِٕۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٞ
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu *suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
* Wannan ãyã tanã nũna yadda wani ke ceton wani sabõda kusanci dõmin a ƙãra daukaka mai ceton. Sharaɗin ceton shĩ ne wanda ake ceton yanã da nãsa ĩmanin. Wanda jinginarsa ta halaka bãbu mai cetonsa. Zuriya ta haɗa uwãye da almajiran mãlami sãlihi. Suna shiga a cikin cetonsa.

22 - At-Tur (The Mount) - 022

وَأَمۡدَدۡنَٰهُم بِفَٰكِهَةٖ وَلَحۡمٖ مِّمَّا يَشۡتَهُونَ
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.

23 - At-Tur (The Mount) - 023

يَتَنَٰزَعُونَ فِيهَا كَأۡسٗا لَّا لَغۡوٞ فِيهَا وَلَا تَأۡثِيمٞ
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.

24 - At-Tur (The Mount) - 024

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ غِلۡمَانٞ لَّهُمۡ كَأَنَّهُمۡ لُؤۡلُؤٞ مَّكۡنُونٞ
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.

25 - At-Tur (The Mount) - 025

وَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.

26 - At-Tur (The Mount) - 026

قَالُوٓاْ إِنَّا كُنَّا قَبۡلُ فِيٓ أَهۡلِنَا مُشۡفِقِينَ
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."

27 - At-Tur (The Mount) - 027

فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيۡنَا وَوَقَىٰنَا عَذَابَ ٱلسَّمُومِ
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."

28 - At-Tur (The Mount) - 028

إِنَّا كُنَّا مِن قَبۡلُ نَدۡعُوهُۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡبَرُّ ٱلرَّحِيمُ
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."

29 - At-Tur (The Mount) - 029

فَذَكِّرۡ فَمَآ أَنتَ بِنِعۡمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٖ وَلَا مَجۡنُونٍ
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.

30 - At-Tur (The Mount) - 030

أَمۡ يَقُولُونَ شَاعِرٞ نَّتَرَبَّصُ بِهِۦ رَيۡبَ ٱلۡمَنُونِ
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?

31 - At-Tur (The Mount) - 031

قُلۡ تَرَبَّصُواْ فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ ٱلۡمُتَرَبِّصِينَ
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."

32 - At-Tur (The Mount) - 032

أَمۡ تَأۡمُرُهُمۡ أَحۡلَٰمُهُم بِهَٰذَآۚ أَمۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?

33 - At-Tur (The Mount) - 033

أَمۡ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥۚ بَل لَّا يُؤۡمِنُونَ
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.

34 - At-Tur (The Mount) - 034

فَلۡيَأۡتُواْ بِحَدِيثٖ مِّثۡلِهِۦٓ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.

35 - At-Tur (The Mount) - 035

أَمۡ خُلِقُواْ مِنۡ غَيۡرِ شَيۡءٍ أَمۡ هُمُ ٱلۡخَٰلِقُونَ
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?

36 - At-Tur (The Mount) - 036

أَمۡ خَلَقُواْ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.

37 - At-Tur (The Mount) - 037

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمۡ هُمُ ٱلۡمُصَۜيۡطِرُونَ
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?

38 - At-Tur (The Mount) - 038

أَمۡ لَهُمۡ سُلَّمٞ يَسۡتَمِعُونَ فِيهِۖ فَلۡيَأۡتِ مُسۡتَمِعُهُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.

39 - At-Tur (The Mount) - 039

أَمۡ لَهُ ٱلۡبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلۡبَنُونَ
Shin, Yanã da* 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
* Waɗansu Lãrãbawa sunãkiran Malã'ika 'ya'yan Allah mãtã, sunã kuma bauta musu dõmin su cece su daga Allah, suna yin gumãka da sũnansu.

40 - At-Tur (The Mount) - 040

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?

41 - At-Tur (The Mount) - 041

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?

42 - At-Tur (The Mount) - 042

أَمۡ يُرِيدُونَ كَيۡدٗاۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هُمُ ٱلۡمَكِيدُونَ
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.

43 - At-Tur (The Mount) - 043

أَمۡ لَهُمۡ إِلَٰهٌ غَيۡرُ ٱللَّهِۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشۡرِكُونَ
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!

44 - At-Tur (The Mount) - 044

وَإِن يَرَوۡاْ كِسۡفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطٗا يَقُولُواْ سَحَابٞ مَّرۡكُومٞ
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.

45 - At-Tur (The Mount) - 045

فَذَرۡهُمۡ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي فِيهِ يُصۡعَقُونَ
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.

46 - At-Tur (The Mount) - 046

يَوۡمَ لَا يُغۡنِي عَنۡهُمۡ كَيۡدُهُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.

47 - At-Tur (The Mount) - 047

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ عَذَابٗا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.

48 - At-Tur (The Mount) - 048

وَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعۡيُنِنَاۖ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnun Mu, kuma ka tsarkake* Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
* (Ma'anar ita ce tsarkakewa kõ tasbĩhi, 'tsare sallõli, farillai, anã cewa' faɗin "Subhãnal lãhi wal Hamdu Lillãhi" a bãyan kõwane mazauni, dõmin ya zama kaffãrar wannan mazaunin.

49 - At-Tur (The Mount) - 049

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَإِدۡبَٰرَ ٱلنُّجُومِ
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) da lõkacin jũyãwar taurãri.

Scroll to Top