الذاريات

 

Adh-Dhariyat

 

The Winnowing Winds

1 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 001

وَٱلذَّـٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

2 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 002

فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

3 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 003

فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.

4 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 004

فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

5 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 005

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

6 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 006

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

7 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 007

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).

8 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 008

إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

9 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 009

يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

10 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 010

قُتِلَ ٱلۡخَرَّـٰصُونَ
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.

11 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 011

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.

12 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 012

يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"

13 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 013

يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.

14 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 014

ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."

15 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 015

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.

16 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 016

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).

17 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 017

كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.

18 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 018

وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.

19 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 019

وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.

20 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 020

وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.

21 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 021

وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?

22 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 022

وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

23 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 023

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,

24 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 024

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

25 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 025

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"

26 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 026

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

27 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 027

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

28 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 028

فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

29 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 029

فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"

30 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 030

قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

31 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 031

۞قَالَ فَمَا خَطۡبُكُمۡ أَيُّهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"

32 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 032

قَالُوٓاْ إِنَّآ أُرۡسِلۡنَآ إِلَىٰ قَوۡمٖ مُّجۡرِمِينَ
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.

33 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 033

لِنُرۡسِلَ عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن طِينٖ
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).

34 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 034

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلۡمُسۡرِفِينَ
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."

35 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 035

فَأَخۡرَجۡنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

36 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 036

فَمَا وَجَدۡنَا فِيهَا غَيۡرَ بَيۡتٖ مِّنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.

37 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 037

وَتَرَكۡنَا فِيهَآ ءَايَةٗ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.

38 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 038

وَفِي مُوسَىٰٓ إِذۡ أَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

39 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 039

فَتَوَلَّىٰ بِرُكۡنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٞ
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"

40 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 040

فَأَخَذۡنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٞ
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

41 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 041

وَفِي عَادٍ إِذۡ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلۡعَقِيمَ
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

42 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 042

مَا تَذَرُ مِن شَيۡءٍ أَتَتۡ عَلَيۡهِ إِلَّا جَعَلَتۡهُ كَٱلرَّمِيمِ
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

43 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 043

وَفِي ثَمُودَ إِذۡ قِيلَ لَهُمۡ تَمَتَّعُواْ حَتَّىٰ حِينٖ
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"

44 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 044

فَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَهُمۡ يَنظُرُونَ
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.

45 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 045

فَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ مِن قِيَامٖ وَمَا كَانُواْ مُنتَصِرِينَ
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.

46 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 046

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.

47 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 047

وَٱلسَّمَآءَ بَنَيۡنَٰهَا بِأَيۡيْدٖ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.

48 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 048

وَٱلۡأَرۡضَ فَرَشۡنَٰهَا فَنِعۡمَ ٱلۡمَٰهِدُونَ
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

49 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 049

وَمِن كُلِّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَا زَوۡجَيۡنِ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.

50 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 050

فَفِرُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

51 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 051

وَلَا تَجۡعَلُواْ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

52 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 052

كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُواْ سَاحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٌ
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."

53 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 053

أَتَوَاصَوۡاْ بِهِۦۚ بَلۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.

54 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 054

فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٖ
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

55 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 055

وَذَكِّرۡ فَإِنَّ ٱلذِّكۡرَىٰ تَنفَعُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.

56 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 056

وَمَا خَلَقۡتُ ٱلۡجِنَّ وَٱلۡإِنسَ إِلَّا لِيَعۡبُدُونِ
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.

57 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 057

مَآ أُرِيدُ مِنۡهُم مِّن رِّزۡقٖ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطۡعِمُونِ
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.*
* Bã Ni nufin su sãmo Mini abinci, kuma bã Ni nufin su dafa Mini abinci.

58 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 058

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلۡقُوَّةِ ٱلۡمَتِينُ
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

59 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 059

فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ ذَنُوبٗا مِّثۡلَ ذَنُوبِ أَصۡحَٰبِهِمۡ فَلَا يَسۡتَعۡجِلُونِ
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.

60 - Adh-Dhariyat (The Winnowing Winds) - 060

فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن يَوۡمِهِمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.

Scroll to Top