الفيل
Al-Fil
The Elephant
1 - Al-Fil (The Elephant) - 001
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ
Ashe, ba ka ga yadda Ubangijin ka Ya aikata ga mutanen giwa* ba?
* An yi Yãƙin Gĩwa shekarar haihuwar Annabi tsakãnin halaka su da haihuwarsa kwãna hamsin. Bayan shekara arba'in Annabi ya fara karantar da mutane. Ya karantar da su cikin shekara ashirin da uku, sa'an nan ya ƙaura. Bayansa da shekara hamsin waanda suka bi shi suka cinye duniya. Wannan yana nuna cewa mutane ba su samun daraja sai da riƙon addini da ilimi.
2 - Al-Fil (The Elephant) - 002
أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ
Ashe, bai sanya kaidin su a cikin ɓata ba?
3 - Al-Fil (The Elephant) - 003
وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ
Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.
4 - Al-Fil (The Elephant) - 004
تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ
Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.
5 - Al-Fil (The Elephant) - 005