”
#65016HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Hakim Dan Hizam - Allah Ya yarda da shi - ya ce:: Na ce: Ya Manzon Allah, kana ganin abubuwan da nake ibada da su a lokacin Jahiliyya na sadaka ko 'yantawa, da sada zumunci, shin a akwai lada? Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a agre shi - ya ce: "Ka m…
”
#65018HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Sufyan Dan Abdullah AlSakafi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ce: Ya Manzon Allah, Ka fadamin wata magana a Musulunci da ba zan tambayi waninka game da ita ba, ya ce: "Ka ce na yi imani da Allah, sannan ka tabbatu akan hakan".
”
#65019HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Dan Umar - Allah Ya yarda da su - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: 'Misalin munafiki, kamar akuya ce mai kaikawo tsakanin turke biyu, tana kaikawo gurin wadannan wani lokaci da kuma zuwa wadancan a wani lokacin".
”
#65020HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abdullahi Dan Amr Dan Aas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai imani yana tsufa a zukatan dayanku kamar yadda tsohon tufafi yake tsufa, ku roki Allah Ya sabunta imani a cikin zukatanku".
”
#65021HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wallahi zan zantar daku wani hadisin da na ji shi daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - wanina ba zai zantar daku shi ba: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa:…
”
#65022HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Alkiyama ba za ta tsaya ba har sai mutum ya wuce wani kabari sai ya ce: Ina ma dai ni ne a wurin nan".
”
#65023HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Alkiyama ba zata ta shi ba har sai kun yaki Yahudawa, har sai dutsen da a bayansa akwai bayahude ya ce: Ya kai Musulmi, wannan bayahude ne ka kashe shi".
”
#65025HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa, Ibnu Maryam (Annabi Isa) ya kusa ya sauka a cikinku yana mai hukunci mai adalci, sai ya karya gicciyayye (cr…
”
#65026HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Lallai cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Alkiyama ba zata tashi ba har sai rana ta bullo ta mafadarta, idan ta bullo mutane suka ganta sai su yi imani gaba dayansu, wannan yayin da: {Wan…
”
#65027HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Alkiyama ba zata tsaya ba har sai zamani ya kusantowa juna, sai shekara ta zama kamar wata, wata kuma ya zama kamar Juma'a (sati guda), Juma'a kuma ta…
”
#65028HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Allah Zai damke kasa, Zai ninke sammai da hannunSa na dama, sannan Ya ce: Ni ne sarki, ina sarakunan kasa".
”
#65030HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abdullahi Dan Amr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Tafkina tafiyar wata ne, ruwansa ya fi nono fari, kamshinsa ya fi almiski kanshi, kofunansa kamar taurarin sama ne, wanda ya sha daga gare shi ba zai y…