”
#3107HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira Allah - Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Idan ka ce wa abokinka: Yi shiru, a ranar Juma'a, a lokacin liman yana huɗuba, to, haƙiƙa ka yi zance mara anfani".
”
#5205HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga jabir dan Abdullahi- Allah ya kara yarda a garesu su biyun- ya ce: { Wani mutum ya zo a lokacin annabi- mai tsira da amincin Allah su kara tabbata a gareshi- yana yiwa mutane huduba a ranar juma`a. sai ya ce: kayi salla ne ya kai wane? sai ya ce: a`a, sai annabi ya…
”
#5393HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya yi wanka irin wankan janaba a ranar Juma`a, sannan ya tafi, kamar ya bayar da sadakar rakuma ne, wanda ya tafi a lokaci na biyu, kamar ya bayar…
”
#5394HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - yana cewa: "Wanda zai je Juma'a a cikinku to ya yi wanka".
”
#5398HadeethEnc[Ingantacce ne]
A kan Salama Bin Al-Akwaa - yardar Allah ta tabbata a gare shi - kuma yana daya daga cikin masu wannan itaciyar da suka ce: "Mun kasance muna yin Sallah tare da Manzon Allah - Salatin Allah da amincin Allah su tabbata a gare shi - sallar Juma'a, sannan muka tashi, kuma…
”
#5399HadeethEnc[Ingantacce ne duka Riwayoyin nasa guda biyun]
An karbo daga Abdullahi dan umar dan khaddabi- Allah ya kara yarda a gare su su biyun- ya ce: { Annabi tsira da aminci su kara tabbata a gareshi ya kasance yana yin hudubobi guda biyu yana zama a tsakanin su } a wata ruwayar ta jabir- Allah ya kara masa yarda-: { manzon…
”
#5433HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya yi alwala sai ya kyautata alwala sannan ya zo Juma'a sai ya saurari huduba kuma ya yi shiru za'a gafarta masa abinda ke tsakaninsa da tsakanin…
”
#5817HadeethEnc[Ingantacce ne]
An rawaito daga Abdullahi Jabir Bn Samarah -Allah ya yarda da su- ya ce:"Na kasance ina Sallah tare da Annabi -Amincin Allah a gare shi- Salloli Sallarsa ta kasance tsakatsaki ce haka Hudubarsa tsakatsaki ce"
”
#8955HadeethEnc[Hasan ne]
An rawaito daga Ali Bn Abu Dalib -Allah ya yarda da shi- "Cewa Annabi ya hana Auren Mutu'a a Ranar yakin Khaibara, da kuma cin Naman Jakin gida"
”
#10035HadeethEnc[Hasan ne]
Daga Samra - Allah ya yarda da shi - tare da marfuu: "Wanda ya yi alwala a ranar Juma'a kuma ya sanya albarka a cikinta, kuma wanda ya yi alwala shi ne mafi alheri."
”
#10036HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Amr Dan Sulaim Al-Ansari ya ce: Na shaida Abu sa'id ya ce: Na shaida Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanka ranar Juma'a wajibi ne akan kowanne baligi, kuma ya yi asuwaki, ya shafa tirare in ya samu".
”
#10551HadeethEnc[Ingantacce ne]
Daga Abu Hurairah - Allah ya yarda da shi - ya ce: Annabi mai tsira da amincin Allah ya ce: “Idan ranar Juma’a mala’iku suka tsaya a kofar masallaci, za su rubuta na farko, sannan na farko. Sannan kwai, kuma idan liman ya fito, sai su nade takardu su saurari zikir…