Allah yayi gaskiya, Kuma cikin Xan Uwanka ya yi Qarya, ka bashi Zuma
Daga Abu Sa`id al-Khudri - yardar Allah ta tabbata a gare shi - cewa wani mutum ya zo wurin Annabi -SAW- ya ce: “Dan’uwana ya koka game da cikinsa, sai ya ce: “Ba shi zuma.” Sai ya zo na biyu ya ce: “Ka ba shi zuma.” Sai ya zo na uku wurinsa sai ya ce: “Ka ba shi zuma.”…

