ya ku mutane, kawai na aikata haka ne don ku yi koyi da ni, kuma ku san sallata
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abu Hazim Dan Dinar Lallai wasu mutane sun zo wa Sahlu ɗan Sa'ad Al-sa'idiy alhali sun yi musu a sha'anin minbarin (Manzon Allah) katakwayensa na mene ne, sai suka tambaye shi game da hakan, sai ya ce: Na rantse da Allah ni na san na mene ne su, haƙiƙa na gan shi a farkon ranar da aka ajiye shi, da kuma farkon ranar da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya fara zama a kansa, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aika zuwa ga wance - wata mace daga Mutanen Madina -Sahlu ya ambace ta -; "Ki umarci yaronki kafinta ya haɗa min katakwaa da zan zauna a kansu idan zanyiwa mutane magana". Sai ta umarce shi sai ya yisu daga bishiyoyin daji, sannan ya zo da su, sai ta aika zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ya yi umarni aka ajiyesu a nan, sannan na ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi sallah a kansu ya yi kabbara alhali yana kansu, sannan ya yi ruku'u alahali yana kansu, sannan ya sauko da baya, sai ya yi sujjada a asalin minbarin sannan ya dawo, yayin da ya gama sai ya fuskanci mutane sai ya ce: "ya ku mutane, kawai na aikata haka ne don ku yi koyi da ni, kuma ku san sallata".
Explanation
Benefits
Halaccin sallah a kan minbari don koyarwa, da halaccin ɗaukakar liman ga mamu don buƙata.
Halaccin neman taimako da masu sana'o'i a buƙatun musulmai.
Halaccin motsi kaɗan a sallah don buƙata.
Halaccin kallon mamu zuwa limaminsa a sallah; don ya koya daga gare shi , kuma hakan ba ya kore khushu'i.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

