Na ga Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi lokacin da yazo Makka in ya sumbaci Arruknul Aswad -farkon dawafi- yana sauri a zagaye uku.
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abdullahi Dan Umar -Allah ya yarda dasu- yace: "Manzo Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi ya yi tamattu'i a Hajjinsa ta bankwana yayi umara yayi hajji kuma yayi hadaya. Ya taho da abin hadayar daga Zulhulaifa. Sai Manzon Allah -tsira da amincin Allah- ya fara yin umara, sannan yayi hajji, sai mutane suka yi tamattu'i tare da Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi suka fara yin umara sannan hajji, daga mutane akwai wanda suka yi hadaya, suka taho da abin hadayar daga Zulhulaifa, wasu kuma basu yi hadayar ba, yayin da Manzon Allah tsira da aminci yazo sai yace da mutane Duk wanda yayi hadaya a cikinku, to duk abin da ya haramta a gare shi to baya halarta har sai ya gama hajjinsa, wanda kuma bai yi hadaya ba to yayi dawafi yayi safa da marwa, ya rage gashi, sannan ya kwance, sannan ya yi hajji kuma ya yi hadaya, wanda bai sami abin yin hadaya ba to yayi azumi uku lokacin hajji ko yayi bakwai idan ya koma garinsu, sai Manzo -tsira da aminci su tabbata a gare shi- yayi dawafi yayin da yazo Makka, ya sumbaci Rukni da farko, sannan yayi dawafi uku da sauri, sauran hudun kuma yayi tafiya a cikinsu, yayi salla raka'a biyu a Makama Ibrahim bayan ya gama dawafinsa, sannan ya yi Safa da Marwa sau bakwai, sannan bai yi wani abu da ya haramta a gare shi ba har sai da ya kammala hajjinsa, ya soke hadaya a ranar sokewa, kuma yayi Dawafin Ifadwa, sannan ya halarta duk abin da ya haramta gare shi a halin gabatar da ibadar, sai wadanda sukayi hadaya suka yi irin duk abin da Manzo -tsira da amincin Allah- ya aikata, "Na ga Manzon Allah -tsira da aminci su tabbata a gare shi lokacin da yazo Makka in ya sumbaci Arruknul Aswad -farkon dawafi- yana sauri a zagaye uku".
Explanation
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

