Lallai haƙiƙa Allah Ya wajabta mata Aljanna da shi, ko kuma Ya 'yanta ta daga wuta da shi
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Nana Aisha Uwar Muminai - Allah Ya yarda da ita - ta ce : Wata miskiniya ta zo wurina tana ɗauke da 'ya'yanta mata biyu, sai na ciyar da ita dabinai uku, sai ta ba wa kowacce ɗaya daga cikinsu su biyun dabinon, sai ta ɗaga dabino zuwa bakinta don ta ci, sai 'ya'yan na ta mata biyun suka nemi ƙara ci daga gareta, sai ta raba musu dabinon da ta so ta ci a tsakaninsu, sai sha'anin ta ya ƙayatar da ni, sai na gaya wa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - abin da ta aikata, sai ya ce: «Lallai haƙiƙa Allah Ya wajabta mata Aljanna da shi, ko kuma Ya 'yanta ta daga wuta da shi».
Explanation
Benefits
Tsananin jin ƙan iyaye mata ga 'ya'yansu da kuma jin tsoron tozarci garesu.
Falalar fifita wani akan kai, da kuma jin ƙan yara ƙana, da ƙarin kyautatawa da kuma rangwami ga 'ya'ya mata, kuma cewa hakan sababi ne na shiga aljanna da kuma 'yantuwa daga wuta.
Kaɗan ba ya hana a yi sadaka da shi saboda ƙanƙantarsa, kai yana kamata ga mai yin sadaka ya yi sadaka da abinda ya sawwaƙa gare shi ya ƙaranta ne ko yana da yawa.
A cikinsa akwai bayanin abinda ɗakunan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suke akai kuma ya rayuwarsa take tare da iyalansa alhali a cikin gidansu babu abinda za'a ci inba dabino ba ko dabinai uku.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

