التين
At-Tin
The Fig
1 - At-Tin (The Fig) - 001
وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ
Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.*
* Ibn Abbas ya ce: 'Attinu shi ne masallacin Nuhu a kan Judiyyi, Azzaitun Masallacin Baitil Muƙaddas.'.
2 - At-Tin (The Fig) - 002
وَطُورِ سِينِينَ
Da Dũr Sĩnĩna.*
* Dutsen da Allah Ya yi magana da Musa a kansa. Ma'anarsa dutse mai albarka sabõda itacen da ke kansa.
3 - At-Tin (The Fig) - 003
وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ
Da wannan gari* amintacce.
* Gari amintacce shi ne Makkah.
4 - At-Tin (The Fig) - 004
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ
Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.
5 - At-Tin (The Fig) - 005
ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ
Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni
6 - At-Tin (The Fig) - 006
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ
Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.
7 - At-Tin (The Fig) - 007
فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ
To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?
8 - At-Tin (The Fig) - 008