الشمس

 

Ash-Shams

 

The Sun

1 - Ash-Shams (The Sun) - 001

وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

2 - Ash-Shams (The Sun) - 002

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
Kuma da wata idan ya bi ta.

3 - Ash-Shams (The Sun) - 003

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

4 - Ash-Shams (The Sun) - 004

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

5 - Ash-Shams (The Sun) - 005

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
Da sama da abin da ya gina ta.

6 - Ash-Shams (The Sun) - 006

وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

7 - Ash-Shams (The Sun) - 007

وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا
Da rai da abin da ya daidaita shi.

8 - Ash-Shams (The Sun) - 008

فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا
Sa'an nan ya yi masa Ilhamar fãjircinsa da shiryuwarsa.

9 - Ash-Shams (The Sun) - 009

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
Lalle ne wanda ya tsarkake* shi (rai) ya sãmi babban rabo.
* Karɓar imãni da aiki da abinda ya ƙunsa tsarkake rai ne.

10 - Ash-Shams (The Sun) - 010

وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe* shi (da laifi) ya tãɓe.
* Kãfirci turbuɗe rai ne da zunubi.

11 - Ash-Shams (The Sun) - 011

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

12 - Ash-Shams (The Sun) - 012

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

13 - Ash-Shams (The Sun) - 013

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

14 - Ash-Shams (The Sun) - 014

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

15 - Ash-Shams (The Sun) - 015

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).

Scroll to Top