الزلزلة

 

Az-Zalzalah

 

The Earthquake

1 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 001

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

2 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 002

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

3 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 003

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

4 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 004

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

5 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 005

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

6 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 006

يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

7 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 007

فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

8 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 008

وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.

Scroll to Top