الزلزلة
Az-Zalzalah
The Earthquake
1 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 001
إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
2 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 002
وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
3 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 003
وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
4 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 004
يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
5 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 005
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
6 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 006
يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
7 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 007
فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
8 - Az-Zalzalah (The Earthquake) - 008