الضحى

 

Ad-Duhaa

 

The Morning Hours

1 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 001

وَٱلضُّحَىٰ
Inã rantsuwa da hantsi.

2 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 002

وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).

3 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 003

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.

4 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 004

وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ
Kuma lalle ta ƙarshe* ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
* Ta ƙarshe, wãto, Lãhira; kuma ta farko, wato, dũniya.

5 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 005

وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.

6 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 006

أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?

7 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 007

وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?

8 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 008

وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?

9 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 009

فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.

10 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 010

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.

11 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 011

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).

Scroll to Top