الضحى
Ad-Duhaa
The Morning Hours
1 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 001
وَٱلضُّحَىٰ
Inã rantsuwa da hantsi.
2 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 002
وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
3 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 003
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
4 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 004
وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ
Kuma lalle ta ƙarshe* ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
* Ta ƙarshe, wãto, Lãhira; kuma ta farko, wato, dũniya.
5 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 005
وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
6 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 006
أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
7 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 007
وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
8 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 008
وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
9 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 009
فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
10 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 010
وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
11 - Ad-Duhaa (The Morning Hours) - 011