التكوير

 

At-Takwir

 

The Overthrowing

1 - At-Takwir (The Overthrowing) - 001

إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ
Idan rãna aka shafe haskenta

2 - At-Takwir (The Overthrowing) - 002

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

3 - At-Takwir (The Overthrowing) - 003

وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ سُيِّرَتۡ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

4 - At-Takwir (The Overthrowing) - 004

وَإِذَا ٱلۡعِشَارُ عُطِّلَتۡ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.

5 - At-Takwir (The Overthrowing) - 005

وَإِذَا ٱلۡوُحُوشُ حُشِرَتۡ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

6 - At-Takwir (The Overthrowing) - 006

وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ سُجِّرَتۡ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

7 - At-Takwir (The Overthrowing) - 007

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ
Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.
* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.

8 - At-Takwir (The Overthrowing) - 008

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ
Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.
* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.

9 - At-Takwir (The Overthrowing) - 009

بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

10 - At-Takwir (The Overthrowing) - 010

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

11 - At-Takwir (The Overthrowing) - 011

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتۡ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

12 - At-Takwir (The Overthrowing) - 012

وَإِذَا ٱلۡجَحِيمُ سُعِّرَتۡ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

13 - At-Takwir (The Overthrowing) - 013

وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

14 - At-Takwir (The Overthrowing) - 014

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

15 - At-Takwir (The Overthrowing) - 015

فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.
* Masu tafiya suna kõmawa bãya.

16 - At-Takwir (The Overthrowing) - 016

ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ
Mãsu gudu suna ɓũya.

17 - At-Takwir (The Overthrowing) - 017

وَٱلَّيۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ
Da dare idan ya bãyar da bãya.

18 - At-Takwir (The Overthrowing) - 018

وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

19 - At-Takwir (The Overthrowing) - 019

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

20 - At-Takwir (The Overthrowing) - 020

ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي ٱلۡعَرۡشِ مَكِينٖ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

21 - At-Takwir (The Overthrowing) - 021

مُّطَاعٖ ثَمَّ أَمِينٖ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

22 - At-Takwir (The Overthrowing) - 022

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجۡنُونٖ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

23 - At-Takwir (The Overthrowing) - 023

وَلَقَدۡ رَءَاهُ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡمُبِينِ
Kuma lalle ne, yã gan shi* a cikin sararin sama mabayyani.
* Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.

24 - At-Takwir (The Overthrowing) - 024

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلۡغَيۡبِ بِضَنِينٖ
Kuma shi, ga gaibi* bã mai rowa ba ne.
* Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.

25 - At-Takwir (The Overthrowing) - 025

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٖ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

26 - At-Takwir (The Overthrowing) - 026

فَأَيۡنَ تَذۡهَبُونَ
Shin, a inã zã ku tafi?

27 - At-Takwir (The Overthrowing) - 027

إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

28 - At-Takwir (The Overthrowing) - 028

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَسۡتَقِيمَ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

29 - At-Takwir (The Overthrowing) - 029

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

Scroll to Top