القلم
Al-Qalam
The Pen
1 - Al-Qalam (The Pen) - 001
نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
2 - Al-Qalam (The Pen) - 002
مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
3 - Al-Qalam (The Pen) - 003
وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
4 - Al-Qalam (The Pen) - 004
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
5 - Al-Qalam (The Pen) - 005
فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
6 - Al-Qalam (The Pen) - 006
بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ
Ga wanenku haukã take.
7 - Al-Qalam (The Pen) - 007
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkin Sa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
8 - Al-Qalam (The Pen) - 008
فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
9 - Al-Qalam (The Pen) - 009
وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
10 - Al-Qalam (The Pen) - 010
وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
11 - Al-Qalam (The Pen) - 011
هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
12 - Al-Qalam (The Pen) - 012
مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
13 - Al-Qalam (The Pen) - 013
عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
14 - Al-Qalam (The Pen) - 014
أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
15 - Al-Qalam (The Pen) - 015
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan ana karanta masa ãyõyin Mu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
16 - Al-Qalam (The Pen) - 016
سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
17 - Al-Qalam (The Pen) - 017
إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
18 - Al-Qalam (The Pen) - 018
وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
19 - Al-Qalam (The Pen) - 019
فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
20 - Al-Qalam (The Pen) - 020
فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
21 - Al-Qalam (The Pen) - 021
فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
22 - Al-Qalam (The Pen) - 022
أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
23 - Al-Qalam (The Pen) - 023
فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
24 - Al-Qalam (The Pen) - 024
أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
25 - Al-Qalam (The Pen) - 025
وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
26 - Al-Qalam (The Pen) - 026
فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
27 - Al-Qalam (The Pen) - 027
بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
28 - Al-Qalam (The Pen) - 028
قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
29 - Al-Qalam (The Pen) - 029
قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
30 - Al-Qalam (The Pen) - 030
فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
31 - Al-Qalam (The Pen) - 031
قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
32 - Al-Qalam (The Pen) - 032
عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
33 - Al-Qalam (The Pen) - 033
كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ
Haka dai azãbar* take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
* Irin wannan azãba ce za a yi wa Ƙuraishãwa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi wa mãsu gonar lambu, wãto da suka tũba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka sãba sãmu. Wato an gayã wa Annabi ne lõkacin da danginsa suka kangare, suka ƙi shiga Musulunci, aka yi musu azãbar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa cewa, zã su musulunta, alheri ya kõma musu. Ya kuwa kõma, kamar yadda Allah Ya yi alkawari
34 - Al-Qalam (The Pen) - 034
إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
35 - Al-Qalam (The Pen) - 035
أَفَنَجۡعَلُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ كَٱلۡمُجۡرِمِينَ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
36 - Al-Qalam (The Pen) - 036
مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
37 - Al-Qalam (The Pen) - 037
أَمۡ لَكُمۡ كِتَٰبٞ فِيهِ تَدۡرُسُونَ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
38 - Al-Qalam (The Pen) - 038
إِنَّ لَكُمۡ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
39 - Al-Qalam (The Pen) - 039
أَمۡ لَكُمۡ أَيۡمَٰنٌ عَلَيۡنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّ لَكُمۡ لَمَا تَحۡكُمُونَ
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kan Mu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
40 - Al-Qalam (The Pen) - 040
سَلۡهُمۡ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
41 - Al-Qalam (The Pen) - 041
أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَآءُ فَلۡيَأۡتُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
42 - Al-Qalam (The Pen) - 042
يَوۡمَ يُكۡشَفُ عَن سَاقٖ وَيُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujada, sai bã zã su iyãwa ba.
43 - Al-Qalam (The Pen) - 043
خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ وَقَدۡ كَانُواْ يُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمۡ سَٰلِمُونَ
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
44 - Al-Qalam (The Pen) - 044
فَذَرۡنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِۖ سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
45 - Al-Qalam (The Pen) - 045
وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidi Na mai ƙarfi ne.
46 - Al-Qalam (The Pen) - 046
أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
47 - Al-Qalam (The Pen) - 047
أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
48 - Al-Qalam (The Pen) - 048
فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
49 - Al-Qalam (The Pen) - 049
لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
50 - Al-Qalam (The Pen) - 050
فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
51 - Al-Qalam (The Pen) - 051
وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَيُزۡلِقُونَكَ بِأَبۡصَٰرِهِمۡ لَمَّا سَمِعُواْ ٱلذِّكۡرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجۡنُونٞ
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
52 - Al-Qalam (The Pen) - 052