الصافات
As-Saffat
Those who set the Ranks
1 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 001
وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفّٗا
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
2 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 002
فَٱلزَّـٰجِرَٰتِ زَجۡرٗا
Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi.
* Mãsu tsãwa, sũ ne Malamai mãsu sãmun ilmin wa'azi daga Annabãwa waɗanda ke karãtun abin tunãwa daga Allah Ubangijin sammai da ƙasa, Mai bãyar da haske ga rãnã, Mai haskaka taurari mãsu ƙãwãtar da samã kuma su tsare ta daga shaiɗanu. An siffanta rãnã da Annabãwa, Malamai da taurãri, ilmi da haske da sababin ƙawa da shiryarwa da kõrar mãsu ɓarna.
3 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 003
فَٱلتَّـٰلِيَٰتِ ذِكۡرًا
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
4 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 004
إِنَّ إِلَٰهَكُمۡ لَوَٰحِدٞ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
5 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 005
رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَرَبُّ ٱلۡمَشَٰرِقِ
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
6 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 006
إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِزِينَةٍ ٱلۡكَوَاكِبِ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
7 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 007
وَحِفۡظٗا مِّن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ مَّارِدٖ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
8 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 008
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰ وَيُقۡذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٖ
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
9 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 009
دُحُورٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٞ وَاصِبٌ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
10 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 010
إِلَّا مَنۡ خَطِفَ ٱلۡخَطۡفَةَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ ثَاقِبٞ
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
11 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 011
فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَهُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَم مَّنۡ خَلَقۡنَآۚ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّن طِينٖ لَّازِبِۭ
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
12 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 012
بَلۡ عَجِبۡتَ وَيَسۡخَرُونَ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
13 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 013
وَإِذَا ذُكِّرُواْ لَا يَذۡكُرُونَ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
14 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 014
وَإِذَا رَأَوۡاْ ءَايَةٗ يَسۡتَسۡخِرُونَ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
15 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 015
وَقَالُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٌ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
16 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 016
أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
17 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 017
أَوَءَابَآؤُنَا ٱلۡأَوَّلُونَ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
18 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 018
قُلۡ نَعَمۡ وَأَنتُمۡ دَٰخِرُونَ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
19 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 019
فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ فَإِذَا هُمۡ يَنظُرُونَ
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
20 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 020
وَقَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا هَٰذَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
21 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 021
هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
22 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 022
۞ٱحۡشُرُواْ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ وَأَزۡوَٰجَهُمۡ وَمَا كَانُواْ يَعۡبُدُونَ
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
23 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 023
مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهۡدُوهُمۡ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡجَحِيمِ
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
24 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 024
وَقِفُوهُمۡۖ إِنَّهُم مَّسۡـُٔولُونَ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
25 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 025
مَا لَكُمۡ لَا تَنَاصَرُونَ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
26 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 026
بَلۡ هُمُ ٱلۡيَوۡمَ مُسۡتَسۡلِمُونَ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
27 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 027
وَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
28 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 028
قَالُوٓاْ إِنَّكُمۡ كُنتُمۡ تَأۡتُونَنَا عَنِ ٱلۡيَمِينِ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
29 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 029
قَالُواْ بَل لَّمۡ تَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
30 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 030
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيۡكُم مِّن سُلۡطَٰنِۭۖ بَلۡ كُنتُمۡ قَوۡمٗا طَٰغِينَ
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
31 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 031
فَحَقَّ عَلَيۡنَا قَوۡلُ رَبِّنَآۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
32 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 032
فَأَغۡوَيۡنَٰكُمۡ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
33 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 033
فَإِنَّهُمۡ يَوۡمَئِذٖ فِي ٱلۡعَذَابِ مُشۡتَرِكُونَ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
34 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 034
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفۡعَلُ بِٱلۡمُجۡرِمِينَ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
35 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 035
إِنَّهُمۡ كَانُوٓاْ إِذَا قِيلَ لَهُمۡ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسۡتَكۡبِرُونَ
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
36 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 036
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓاْ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٖ مَّجۡنُونِۭ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
37 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 037
بَلۡ جَآءَ بِٱلۡحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
38 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 038
إِنَّكُمۡ لَذَآئِقُواْ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡأَلِيمِ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
39 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 039
وَمَا تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
40 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 040
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
41 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 041
أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ رِزۡقٞ مَّعۡلُومٞ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
42 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 042
فَوَٰكِهُ وَهُم مُّكۡرَمُونَ
Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
43 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 043
فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
44 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 044
عَلَىٰ سُرُرٖ مُّتَقَٰبِلِينَ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
45 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 045
يُطَافُ عَلَيۡهِم بِكَأۡسٖ مِّن مَّعِينِۭ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
46 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 046
بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
47 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 047
لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
48 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 048
وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
49 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 049
كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
50 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 050
فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
51 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 051
قَالَ قَآئِلٞ مِّنۡهُمۡ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٞ
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
52 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 052
يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُصَدِّقِينَ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
53 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 053
أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
54 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 054
قَالَ هَلۡ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
55 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 055
فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِي سَوَآءِ ٱلۡجَحِيمِ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
56 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 056
قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرۡدِينِ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
57 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 057
وَلَوۡلَا نِعۡمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ ٱلۡمُحۡضَرِينَ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
58 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 058
أَفَمَا نَحۡنُ بِمَيِّتِينَ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
59 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 059
إِلَّا مَوۡتَتَنَا ٱلۡأُولَىٰ وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
60 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 060
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
61 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 061
لِمِثۡلِ هَٰذَا فَلۡيَعۡمَلِ ٱلۡعَٰمِلُونَ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
62 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 062
أَذَٰلِكَ خَيۡرٞ نُّزُلًا أَمۡ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
63 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 063
إِنَّا جَعَلۡنَٰهَا فِتۡنَةٗ لِّلظَّـٰلِمِينَ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
64 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 064
إِنَّهَا شَجَرَةٞ تَخۡرُجُ فِيٓ أَصۡلِ ٱلۡجَحِيمِ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
65 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 065
طَلۡعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
66 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 066
فَإِنَّهُمۡ لَأٓكِلُونَ مِنۡهَا فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
67 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 067
ثُمَّ إِنَّ لَهُمۡ عَلَيۡهَا لَشَوۡبٗا مِّنۡ حَمِيمٖ
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
68 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 068
ثُمَّ إِنَّ مَرۡجِعَهُمۡ لَإِلَى ٱلۡجَحِيمِ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
69 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 069
إِنَّهُمۡ أَلۡفَوۡاْ ءَابَآءَهُمۡ ضَآلِّينَ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
70 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 070
فَهُمۡ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ يُهۡرَعُونَ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
71 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 071
وَلَقَدۡ ضَلَّ قَبۡلَهُمۡ أَكۡثَرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
72 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 072
وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
73 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 073
فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
74 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 074
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
75 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 075
وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
76 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 076
وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
77 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 077
وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
78 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 078
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
79 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 079
سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٖ فِي ٱلۡعَٰلَمِينَ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
80 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 080
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
81 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 081
إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai.
82 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 082
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
83 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 083
۞وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبۡرَٰهِيمَ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
84 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 084
إِذۡ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلۡبٖ سَلِيمٍ
A lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
85 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 085
إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَاذَا تَعۡبُدُونَ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
86 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 086
أَئِفۡكًا ءَالِهَةٗ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
87 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 087
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
88 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 088
فَنَظَرَ نَظۡرَةٗ فِي ٱلنُّجُومِ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
89 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 089
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٞ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
90 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 090
فَتَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ مُدۡبِرِينَ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
91 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 091
فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمۡ فَقَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
92 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 092
مَا لَكُمۡ لَا تَنطِقُونَ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
93 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 093
فَرَاغَ عَلَيۡهِمۡ ضَرۡبَۢا بِٱلۡيَمِينِ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
94 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 094
فَأَقۡبَلُوٓاْ إِلَيۡهِ يَزِفُّونَ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
95 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 095
قَالَ أَتَعۡبُدُونَ مَا تَنۡحِتُونَ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
96 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 096
وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
97 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 097
قَالُواْ ٱبۡنُواْ لَهُۥ بُنۡيَٰنٗا فَأَلۡقُوهُ فِي ٱلۡجَحِيمِ
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
98 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 098
فَأَرَادُواْ بِهِۦ كَيۡدٗا فَجَعَلۡنَٰهُمُ ٱلۡأَسۡفَلِينَ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
99 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 099
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهۡدِينِ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
100 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 100
رَبِّ هَبۡ لِي مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
101 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 101
فَبَشَّرۡنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٖ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri.
* Yãron da aka yi bushãra da shi a nan, shĩ ne Ismã'ĩla' sabõda abin da yake tafe a gaba wanda ya shãfi Is'hãƙa da sũnansa a bayyane yã nũna a nan bã shi ba ne. Watau Ismã'ĩla kawai ne.
102 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 102
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعۡيَ قَالَ يَٰبُنَيَّ إِنِّيٓ أَرَىٰ فِي ٱلۡمَنَامِ أَنِّيٓ أَذۡبَحُكَ فَٱنظُرۡ مَاذَا تَرَىٰۚ قَالَ يَـٰٓأَبَتِ ٱفۡعَلۡ مَا تُؤۡمَرُۖ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
103 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 103
فَلَمَّآ أَسۡلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلۡجَبِينِ
Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago
104 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 104
وَنَٰدَيۡنَٰهُ أَن يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
105 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 105
قَدۡ صَدَّقۡتَ ٱلرُّءۡيَآۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
106 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 106
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡبَلَـٰٓؤُاْ ٱلۡمُبِينُ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
107 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 107
وَفَدَيۡنَٰهُ بِذِبۡحٍ عَظِيمٖ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
108 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 108
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
109 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 109
سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
110 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 110
كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
111 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 111
إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
112 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 112
وَبَشَّرۡنَٰهُ بِإِسۡحَٰقَ نَبِيّٗا مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
* Wannan sãbuwar bushãra da Is'hãƙa tanã nũna cewa bã shĩ ne wanda kissar yankã ta shãfa ba sabõda haka Isma'ĩla dai ne tabbas, mai ƙissar yankã. Sabõda haka Allah Ya sanya shi wata al'umma dabam' dõmin a sãka masa, sa'an nan aka sãkawa Ibrãhĩm da Is'hãƙa dõmin ya zama wata al'umma ta dabam,.
113 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 113
وَبَٰرَكۡنَا عَلَيۡهِ وَعَلَىٰٓ إِسۡحَٰقَۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحۡسِنٞ وَظَالِمٞ لِّنَفۡسِهِۦ مُبِينٞ
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
114 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 114
وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
115 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 115
وَنَجَّيۡنَٰهُمَا وَقَوۡمَهُمَا مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
116 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 116
وَنَصَرۡنَٰهُمۡ فَكَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
117 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 117
وَءَاتَيۡنَٰهُمَا ٱلۡكِتَٰبَ ٱلۡمُسۡتَبِينَ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
118 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 118
وَهَدَيۡنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
119 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 119
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِمَا فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
120 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 120
سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
121 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 121
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
122 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 122
إِنَّهُمَا مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle, sunã daga bãyin Mu mũminai.
123 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 123
وَإِنَّ إِلۡيَاسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
124 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 124
إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
125 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 125
أَتَدۡعُونَ بَعۡلٗا وَتَذَرُونَ أَحۡسَنَ ٱلۡخَٰلِقِينَ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
126 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 126
ٱللَّهَ رَبَّكُمۡ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
127 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 127
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
128 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 128
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
129 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 129
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
130 - As-Saffat (Those who set the Ranks) - 130
سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلۡ يَاسِينَ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
131 - As-Saffat (Those