الشعراء

 

Ash-Shu'ara

 

The Poets

1 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 001

طسٓمٓ
T. S̃. M̃.

2 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 002

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

3 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 003

لَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ أَلَّا يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba!
* Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.

4 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 004

إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

5 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 005

وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ مُحۡدَثٍ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهُ مُعۡرِضِينَ
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

6 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 006

فَقَدۡ كَذَّبُواْ فَسَيَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَـٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

7 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 007

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

8 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 008

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

9 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 009

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

10 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 010

وَإِذۡ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئۡتِ ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

11 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 011

قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَۚ أَلَا يَتَّقُونَ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

12 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 012

قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

13 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 013

وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci* kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.

14 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 014

وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

15 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 015

قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

16 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 016

فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

17 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 017

أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

18 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 018

قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

19 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 019

وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

20 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 020

قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin fushi."

21 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 021

فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

22 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 022

وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

23 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 023

قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

24 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 024

قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

25 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 025

قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

26 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 026

قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

27 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 027

قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

28 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 028

قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

29 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 029

قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

30 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 030

قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

31 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 031

قَالَ فَأۡتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

32 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 032

فَأَلۡقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعۡبَانٞ مُّبِينٞ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

33 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 033

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِيَ بَيۡضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

34 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 034

قَالَ لِلۡمَلَإِ حَوۡلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٞ
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

35 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 035

يُرِيدُ أَن يُخۡرِجَكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِۦ فَمَاذَا تَأۡمُرُونَ
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

36 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 036

قَالُوٓاْ أَرۡجِهۡ وَأَخَاهُ وَٱبۡعَثۡ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

37 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 037

يَأۡتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٖ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

38 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 038

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

39 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 039

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلۡ أَنتُم مُّجۡتَمِعُونَ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

40 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 040

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

41 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 041

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُواْ لِفِرۡعَوۡنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجۡرًا إِن كُنَّا نَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

42 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 042

قَالَ نَعَمۡ وَإِنَّكُمۡ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

43 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 043

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلۡقُواْ مَآ أَنتُم مُّلۡقُونَ
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

44 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 044

فَأَلۡقَوۡاْ حِبَالَهُمۡ وَعِصِيَّهُمۡ وَقَالُواْ بِعِزَّةِ فِرۡعَوۡنَ إِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبُونَ
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

45 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 045

فَأَلۡقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلۡقَفُ مَا يَأۡفِكُونَ
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

46 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 046

فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

47 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 047

قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

48 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 048

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

49 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 049

قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَ فَلَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ أَجۡمَعِينَ
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

50 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 050

قَالُواْ لَا ضَيۡرَۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

51 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 051

إِنَّا نَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

52 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 052

۞وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã* ne.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.

53 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 053

فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

54 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 054

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

55 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 055

وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

56 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 056

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

57 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 057

فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

58 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 058

وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ
Da taskõki da mazauni mai kyau.

59 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 059

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

60 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 060

فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

61 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 061

فَلَمَّا تَرَـٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

62 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 062

قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

63 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 063

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,* kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
* Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.

64 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 064

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

65 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 065

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

66 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 066

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

67 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 067

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

68 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 068

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

69 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 069

وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ إِبۡرَٰهِيمَ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

70 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 070

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَا تَعۡبُدُونَ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

71 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 071

قَالُواْ نَعۡبُدُ أَصۡنَامٗا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

72 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 072

قَالَ هَلۡ يَسۡمَعُونَكُمۡ إِذۡ تَدۡعُونَ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

73 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 073

أَوۡ يَنفَعُونَكُمۡ أَوۡ يَضُرُّونَ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

74 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 074

قَالُواْ بَلۡ وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفۡعَلُونَ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

75 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 075

قَالَ أَفَرَءَيۡتُم مَّا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

76 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 076

أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلۡأَقۡدَمُونَ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"

77 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 077

فَإِنَّهُمۡ عَدُوّٞ لِّيٓ إِلَّا رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

78 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 078

ٱلَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهۡدِينِ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

79 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 079

وَٱلَّذِي هُوَ يُطۡعِمُنِي وَيَسۡقِينِ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

80 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 080

وَإِذَا مَرِضۡتُ فَهُوَ يَشۡفِينِ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

81 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 081

وَٱلَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحۡيِينِ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

82 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 082

وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

83 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 083

رَبِّ هَبۡ لِي حُكۡمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّـٰلِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

84 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 084

وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٖ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya* a cikin mutãnen ƙarshe."
* Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci

85 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 085

وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

86 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 086

وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

87 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 087

وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

88 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 088

يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٞ وَلَا بَنُونَ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

89 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 089

إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٖ سَلِيمٖ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

90 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 090

وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

91 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 091

وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

92 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 092

وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

93 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 093

مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

94 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 094

فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ
Sai aka kikkife su* a cikinta, su da halakakkun.
* Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.

95 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 095

وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

96 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 096

قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

97 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 097

تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

98 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 098

إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

99 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 099

وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

100 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 100

فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

101 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 101

وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٖ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

102 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 102

فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

103 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 103

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

104 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 104

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

105 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 105

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

106 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 106

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da Dan uwansu Nuhu ya ce musu, "Bã zã ku ji tsoron Allah ba?"

107 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 107

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."

108 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 108

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

109 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 109

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

110 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 110

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

111 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 111

۞قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

112 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 112

قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

113 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 113

إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

114 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."

115 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 115

إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

116 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 116

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

117 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

118 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 118

فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

119 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 119

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

120 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 120

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

121 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 121

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

122 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

123 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 123

كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

124 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 124

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

125 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 125

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

126 - Ash-Shu'ara (The Poets) - 126

Scroll to Top