Mabuɗan gaibu biyar ne
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Mabuɗan gaibu biyar ne, {Lalle, Allah a wurinSa kawai sanin yaushe Alkiyama zata tashi yake, kuma Yanã saukar da ruwan sama, kuma Yanã sanin abin da yake a cikin mahaiffannai kuma wani rai bai san abin da yake aikatãwa a gõbe ba, kuma wani rai bai san a wace ƙasã yake mutuwa ba. Lalle Allah Masani ne Mai ƙididdidigẽwa}».
Explanation
Benefits
Sindi ya ce: Faɗinsa: (Mabuɗan gaibu guda biyar ne), an ambaci waɗanda biyar ɗin: Mabuɗan gaibu; domin cewa duk wanda yake da waɗannan biyar ɗin to yana da bakiɗayan gaibu, sai suka zama kai kace dasu ne ake buɗe taskokin gaibu.
Ibnu Hajar ya ce: Ibnu Abi Jamra ya ce: Ya ambace su da mabuɗai dan kusanto da al'amarin ga mai ji; domin cewa duk abin da ya sanya shamaki tsakaninka da shi haƙiƙa ya ɓoye maka, kuma kaiwa zuwa ga saninsa a al'ada daga ƙofa ne, idan an kulle ƙofar sai a buƙatu zuwa mabuɗai, idan abin da ba'a tsinkaya akan gaibu sai an kai zuwa gare shi ba'a sanin bigirensa to ta yaya zai san abin da aka ɓoye.
Ibnu Abi jamra ya ce: Hikima cikin sanya su biyar nuni zuwa taƙaita nau'ikan halittu a cikinsu.
Allah - Mai girma da ɗaukaka - Yakan bayyanar da wasu daga cikin gaibu ga manzanni, dan wata hikima daga gareShi.
Ɓata shacifaɗin masana taurari da bokaye a da'awarsu cewa sun san gaibu, kuma wanda ya yi da'awar wani abu daga abin da Allah - tarki ya tabbatar maSa - Ya kaɗaita da saninSa, to haƙiƙa ya ƙaryata Allah - Maɗaukakain sarki - da ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da kuma Alƙur'ani mai girma.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

