Na rantse da wanda ran Muhammad yake a hannunSa, kofunansa sun fi yawan adadin taurarin sama
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abu Zarr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ce: Ya Manzon Allah menene kofunan tafki? (Sai) ya ce: "Na rantse da wanda ran Muhammad yake a hannunSa, kofunansa sun fi yawan adadin taurarin sama ku saurara a cikin duhun daren da babu hazo, kofunan Aljanna wanda ya sha daga garesu ba zai yi kishirwa ba har karshen al’amarinsa (na kishirwa), indararo biyu ne suke zuba a cikinsa daga Aljanna, wanda ya sha daga gareshi Ba zai yi kishirwa ba, fadinsa tamkar tsawonsa ne, tsakanin Amman zuwa Ailata, ruwansa ya fi nono tsananin fari, kuma ya fi zuma zaki".
Explanation
Benefits
Girman tafkin da tsawonsa da fadinsa da yawan kofunan sa.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

