Idan ɗayanku ya haɗu da ɗan uwansa to ya yi masa sallama, idan bishiya ko katanga ko dutse ya tsare tsakaninsu sannan ya haɗu da shi to ya yi masa sallama kuma
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce : "Idan ɗayanku ya haɗu da ɗan uwansa to ya yi masa sallama, idan bishiya ko katanga ko dutse ya tsare tsakaninsu sannan ya haɗu da shi to ya yi masa sallama kuma".
Explanation
Benefits
Tsananin kwaɗayinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - akan yaɗa sunnar sallama da kai matuƙa a cikinta; dan abinda ke cikinta na jawo soyayya da hada tsakanin musulmai.
Sallama ita ce faɗin: Assalamu alaikum, (Aminci ya tabbata a gareku) ko: Assalamu alaikum wa rahmatullah wa barakatuh, wato(Aminci ya tabbata a gareku da rahamar Allah da albarkarSa), banda musafahar da take faruwa alokacin farkon haɗuwa.
Sallama addu'a ce, musulmai suna cikin buƙatuwar junansu su yi wa junansu addu'a koda hakan ya maimaitu.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

