Idan bawa musulmi ya yi alwala - ko kuma mumini - sai ya wanke fuskar sa, to kowane kuskuren da ya yi kallo da shi da idanun sa zai fice daga fuskar sa tare da ruwa - ko kuma tare da ƙarshen ɗigon ruwa
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Lallai cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan bawa musulmi ya yi alwala - ko kuma mumini - sai ya wanke fuskar sa, to kowane kuskuren da ya yi kallo da shi da idanun sa zai fice daga fuskar sa tare da ruwa - ko kuma tare da ƙarshen ɗigon ruwa - idan ya wanke hannayen sa, kowane kuskure zai fita daga hannayen sa waɗanda hannayen sa suka damƙa tare da ruwa - ko tare da ƙarshen ɗigon ruwa -, idan ya wanke ƙafafuwan sa kowane kuskuren da ƙafafuwan sa suka tafi gare shi zasu fita tare da ruwa - ko tare da ƙarshen ɗigon ruwa - har sai ya fita tsarkakakke daga zunubai".
Explanation
Benefits
Daga shiryarwar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi yana kwaɗaitar da mutane a cikin ayyukan ɗa'a da kuma ibadu ta hanyar ambatan lada da sakamako akan su.
Kowace gaɓa daga gaɓɓan mutum tana faɗawa cikin wani abu daga saɓo, saboda haka zunubai suke bin kowace gaɓar da ta aikatasu, kuma suna fita daga kowace gaɓar da ya tuba daga gareta.
Alwala, a cikinta akwai tsarkaka ta gani ɓaro-ɓaro, kuma tana kasancewa ne a lokacin da kake wanke gaɓɓan alwala, da kuma tsarkakewa ta ma'ana tana kasancewa ne daga zunuban da suka faru daga gaɓɓan.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

