Addu'ar musulmi ga ɗan'uwansa a ɓoye abar karɓa ce
Choose an available translation of this Hadeeth
Hadeeth text
Daga Ummu al-Darda'i da Abu al-Darda'i - Allah Ya yarda da su - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbara agare shi - ya kasance yana cewa: «Addu'ar musulmi ga ɗan'uwansa a ɓoye abar karɓa ce, a daidai kansa akwai wani Mala'ika wanda aka wakilta a duk lokacin da ya yi wa ɗan'uwansa addu'a ta alheri, sai Mala'ikan da aka wakilta gare shi ya ce: Amin, kaima (Allah Ya baka) kwatankwacin haka».
Explanation
Benefits
Addu'a a ɓoye tana nuni a bayyane akan gaskiyar imani da kuma 'yan uwantaka.
Ƙayyade addu'a da cewa a ɓoye; domin cewa hakan ya fi kai matuƙa a ikhlasi (wato yi domin Allah) da kuma halartowar zuciya.
Daga cikin sabubban amsa addu'a akwai musulmi ya yi wa ɗan'uwansa musulmi addu'a a ɓoye.
Nawawi ya ce; Falalar addu'a ga ɗan'uwansa musulmi a ɓoye, da a ce zai yi wa jama'ar musulmai addu'a to wannan falalar zata tabbata, da kuma a ce zai yi addu'a ga jumlar musulmai to zance mabayyani shi ne samuwar (falalar), wani daga cikin magabata na gari ya kasance idan yana so ya yi wa kansa addu'a sai ya yi wa ɗan'uwansa addu'a da wannan addu'ar; domin cewa ita za'a amsata, kuma zai samu kwatankwacinta.
Bayanin wasu daga cikin ayyukan Mala'iku, kuma cewa daga cikinsu akwai wanda Allah Ya wakilta shi ga wannan aikin.
Attribution
Categories
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

