HadeethEnc · 1.25.0
Kada ku zagi sahabbaina, da a ce ɗayanku zai ciyar da zinare kwatankwacin dutsen Uhudu ba zai kai cikin mudun ɗayansu ba, ko rabinsa
Available translations
Choose an available translation of this Hadeeth
01
Hadeeth text
Daga Abu Sa'id AlKhudri - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Kada ku zagi sahabbaina, da a ce ɗayanku zai ciyar da zinare kwatankwacin dutsen Uhudu ba zai kai cikin mudun ɗayansu ba, ko rabinsa".
02
Explanation
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana hani daga zagin sahabbai, musamman ma marigaya na farko daga muhajirai da mutanen Madina; kuma ya bada labarin cewa shi da wani daga mutane zai ciyar da kwatankwacin dutsen Uhudu na zinari ladansa ba zai kai ladan ciyarwar wani daga sahabbai ba mudu na abinci ko rabinsa ba - mudu shi ne cikin tafuka biyu na mutum matsakaicin halitta -; hakan dan ƙarin ikhlasinsu, da gaskiyar niyyarsu, da rigayar ciyarwarsu da yaƙinsu kafin buɗe Makka inda tsananin buƙatuwa gare shi take.
03
Benefits
Zagin sahabbai - Allah Ya yarda da su - haramun ne, kuma yana daga manyan zunubai.
Attribution
[Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi]
Categories
Share
Share hadeeth
Sharing options · 0 Total shares

